Friday 2 May 2014

Part 3

Tun lokacin da na fara rubutu akan Mauludin Annabi (s.a.w.w) na hadu da chalenges kala-kala daga maqiyan al'amarin.Wadansu sukan zageni (ta inbox), wasu kuma sukanyi comment a wall dina, suyi ta jayayya da musu akan cewa su basu gamsu da hujjojin ba. Duk da cewa har yanzun ban fadi wani ra'ayi nawa ba, illa dai abubuwan da manyan Maluma suka rubuta a litattafansu.. Kuma dukkansu sukan ciro hujjojinsu ne daga ayoyin Alqur'ani Mai tsarki, tare da tafsirin ayoyin ta hanyar ruwayoyi ingantattu daga manyan Sahabbai.. Amma duk da haka, makiyan Mauludi sai Qara kumfar baki sukeyi.Kasancewar duk hujjojin da nake kawowa sunfi Qarfin turuwa ta kowacce hanya, (tunda ayoyi ne ba hadisai ba. Ballantana mutum yace hadisan basu inganta ba..)Sai suke tambaya ta wai''shin, Sayyiduna Abubakar da Umar da Uthman da Aliyyu (r.t.a) dasu Imamu Malik dss, me yasa su basu yi Mauludi ba? Ko kuwa su basu fahimci wadannan hujjojin naka bane?''To amsa ta ga masu irin wannan tambaya ita ce:1. Asalin kowanne abu a addini, HALAL ne. Komai da Komai. Sai illa abubuwan da shari'a ta haramta.. Ta hanyar ayar Alqur'ani, ko hadisi ingattatce..Sannan kuma addini bai bada damar ka hana wani mutum yin wani abu wanda aka samu sabanin Malamai akansa ba..Saboda haka masu kin Mauludi, idan kuna so mu hanu mu dena, sai dai ku kawo mana hujjar da ta hana yin Mauludi.. Daga Alqur'ani ko hadisi, ko ijma'i..Na san cewar kuna yawan kafa hujja da ''Fa inna kulla muhdathatin bid'ah, wa kulla bid'atin dhalaalah''..To ya kamata kusan cewar wannan kalmar ''KULLU'' din tana zuwa da ma'anoni da yawa a larabci. Tazo awurare da dama amma kuma da ma'anoni mabambanta.Idan kunce Ai Maulidi bidi'a ne,to mu kuma sai mu Qara tunatar daku cewar* Musabaqah ma Bidi'a ce.* Kafa Qungiya ma Bidi'a ne.* Ware Masallaci ma (saboda bambancin Ra'ayi) Bidi'a ce Muharramah.* Sanyawa Masallatai ko Makarantu sunayen Sahabbai ma Bidi'ah ne.* Bikin yaye Dalibai ma Bidi'a ne.Tambaya anan ita ce: Me yasa duk wadannan Bidi'o'in baku yin inkarinsu???Maimakon haka ma sai ku ka daukesu kuke aikatawa Kullum, ku ka Maishe su Sunnoninku???Har ya zamto Mabiyanku basu iya bambancewa Tsakanin Sunnonin Annabin Rahama (saww) a kuma Sunnoninku na Son Zuciya???Me yasa Ranku ba ya baci sai kunga ana Murnar Haihuwar Manzon Allah (saww) ???Anya Wannan ba alamar Munafurci bane???Hatta ita Qasar da take bunkasa wannan Aqeedar Munafurcin aduniya, Ta yarda kuma ta Amince wa Kiristocin Sojojin Amurka da suke girke akasar cewar Su gudanar da Bikin Kirsimati. Amma bata yarda Maluman Sufaye na Qasar Su Gudanar da taron Maulidin Manzon Allah (saww) ba!!!* Sannan dukkan Sarakunan Ita Saudiyyar da Ameerai maza da mata su kan gudanar da Bukukuwan Birthday nasu idan ranar haihuwarsu ta kewayo. Amma me yasa maluman Qasar basu yin inkari??Anya Wannan ba yana Nuna Tsantsar Qiyayya ga Manzon Allah bane acikin zukatansu, alhali abaki suna nuna cewar su mabiya sunnah ne??Ya kamata dai masu kushe harkar Maulidi su fahimci cewar: idan ma an tafi akan cewa bidi'ah ne, to ai bidi'ar ta kasu kashi-kashi.1. Akwai bid'ah muharramah,2. akwai bid'ah wajiba,3. akwai bidi'ah Mandubah,4. akwai bid'ah makruhiyah,5. akwai bidi'a mubahiyah.Don Qarin bayani aje aduba littafin 'IH-YA'US_SUNNA H' na Shaikh Uthman bn Fudiy (r.t.a).Anan za'a ga Matsayin Maulidi.Da fatan wadannan hujjoji nawa zasu gamsar da duk wani mai neman gaskiya..YA Allah KA Qara ganar damu. Allah KA Qara mana SON ANNABI (s.a.w.w).. Ka bamu dukiya mai yawa wacce zamuyi ta hidima da ita abisa JANIBIN SHUGABANMU (s.a.w.w).

No comments:

Post a Comment